Gwamnatin tarayya ta bukaci Ma’aikatan ta masu matakin Albashi na 12 su koma bakin aiki daga ranar 1 ga watan Disamba.
Shugabar Ma’aikatan Gwamnatin tarayya Dr Folasade Yemi-Esan, ita ce ta bayyana hakan, inda ta ce hakan ya biyo bayan umarnin Kwamatin yaki da cutar Corona na Shugaban Kasa.
A wani mataki na rage yaduwar cutar Corona, Gwamnatin tarayya a ranar 4 ga watan Maris ta umarci Ma’aikata masu matakin Albashi na 12 zuwa kasa su fara aiki daga gida.
Bayan Kimanin watanni 8 kenan, gwamnatin tarayya ta umarci Ma’aikata su gabatar da shaidar anyi musu rigakafin cutar Corona cikin a wanni 72 masu zuwa.
Dr Folasade Yemi-Esan, ta bayyana cewa kowanne ma’aikaci ya tabbatar da cewa an mssu rigakafin cutar, kamar yadda Kwamatin Shugaban Kasa kan yaki da cutar Corona ya bukata.