Gwamnatin tarayya ta buƙaci ma’aikatan ta masu matakin albashi na 12 da su koma bakin aiki

0 127

Gwamnatin tarayya ta bukaci Ma’aikatan ta masu matakin Albashi na 12 su koma bakin aiki daga ranar 1 ga watan Disamba.

Shugabar Ma’aikatan Gwamnatin tarayya Dr Folasade Yemi-Esan, ita ce ta bayyana hakan, inda ta ce hakan ya biyo bayan umarnin Kwamatin yaki da cutar Corona na Shugaban Kasa.

A wani mataki na rage yaduwar cutar Corona, Gwamnatin tarayya a ranar 4 ga watan Maris ta umarci Ma’aikata masu matakin Albashi na 12 zuwa kasa su fara aiki daga gida.

Bayan Kimanin watanni 8 kenan, gwamnatin tarayya ta umarci Ma’aikata su gabatar da shaidar anyi musu rigakafin cutar Corona cikin a wanni 72 masu zuwa.

Dr Folasade Yemi-Esan, ta bayyana cewa kowanne ma’aikaci ya tabbatar da cewa an mssu rigakafin cutar, kamar yadda Kwamatin Shugaban Kasa kan yaki da cutar Corona ya bukata.

Leave a Reply

%d bloggers like this: