Gwamnatin tarayya ta kaddamar da wani kwamitin tsakanin ma’aikatu wanda zai lalubo hanyoyin da za abi a rage barnar da ambaliyar ruwa ke jawowa a fadin kasarnan.
Ministar jin kai, kula da annoba da jin dadin jama’a, Sadiya Umar Farouq, wacce ta kaddamar da kwamitin a Abuja, tace kwamitin zai yi aiki tukuru wajen samar da wani shirin kasa na shiryawa annoba da bayar da tallafi.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
Ministar tace hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa NEMA ta samar da hanyoyin kula da ambaliyar ruwa, kuma akwai shirin kai ziyara zuwa ga gwamnatocin jihoshi domin duba yadda aka shirya da kuma bayar da agajin ambaliyar ruwa.
Yace an zakulo yan kwamitin daga ma’aikatar jin kai, kula da annoba da jin dadin jama’a, da ma’aikatar da albarkatun ruwa da ma’aikatar gona da ta muhalli da ma’aikatar cikin gida da ta yada labarai, da sauransu.