Hukumar INEC ta gargadi jam’iyyun siyasa cewa za ta rufe karbar sunayen ‘yan takara na zaben 2023

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC, ta gargadi jam’iyyun siyasa cewa za ta rufe shafin ta internet da ake dora sunayen ‘yan takara a zaben 2023 da karfe 6 na yammacin ranar 17 ga watan Yuni domin zabukan kasa da kuma karfe 6 na yamma ranar 15 ga watan Yuli domin zaben jihohi.

Shugaban hukumar ta INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, ya yi wannan gargadin a taron da hukumar ta yi da kwamishinonin zabe, jiya a Abuja.

Mahmood Yakubu ya tunatar da jam’iyyun siyasa cewa an kammala dukkan zaben fidda gwani na jam’iyyu na shekarar 2023 a jiya, yayin da aka fara dora sunayen ‘yan takara a yau.

Mahmood Yakubu ya kara da cewa, domin cimma wannan buri, an horas da jami’ai hudu da dukkanin jam’iyyun siyasa 18 suka zaba, akan yadda za a rika shigar da fom takara a shafin internet da aka samar.

Ya kuma bayyana cewa, an kafa cibiyar tantance sunayen ‘yan takara a hedikwatar hukumar domin karba da kuma gudanar da dukkan ‘yan takara na jam’iyyun siyasa domin zaben 2023.

Comments (0)
Add Comment