Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta ceto rayuka fiye da 1,000 da dukiyoyi kimanin miliyan 905 daga gobara 867 da aka samu a 2022

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano tace ta ceto rayuka dubu 1 da 35 da dukiyoyi da darajarsu ta kai naira miliyan 905 daga gobara 867 da aka samu a jihar daga watan Janairu zuwa Disambar 2022.

Jami’in hulda da jama’a na hukumar, Saminu Yusuf Abdullahi, shine ya sanar da haka cikin wata sanarwa da ya fitar a Kano.

Sai dai, Yusuf Abdullahi yace mutane 166 sun rasa rayukansu, yayinda aka yi asarar dukiyoyi na naira miliyan 358 a gobara daban-daban cikin shekarar.

Ya kuma ce hukumar ta kai dauki a hatsarin mota guda 575, yayin da ta ceto dabbobi 6 da suka makale.

Kakakin ya danganta gobara da aka samu a daban-daban da sakaci wajen amfani da gas na girki da kuma amfani da kayan wuta marasa inganci.

Ya shawarci jama’a da su kauracewa ajiye fetur a gida ko duk wani waje mara tsaro saboda karancin man fetur.

Yusuf Abdullahi ya kuma shawarci mazauna jihar da suke kiran hukumar idan suna bukatar daukin gaggawa.

Comments (0)
Add Comment