Asusun kiwon lafiya na jihar Jigawa yace kawo yanzu asibitoci masu zaman kansu guda 10 ne suka nuna sha’awarsu ta shiga shirin asusun adashen gata na kiwon lafiya na jiha.
Sakataren zartarwa na asusun Dr Nura Ibrahim ya sanar da haka ga Radio Jigawa.
Yace daga cikin asibitocin masu zaman kansu da suka yi rijistar shiga shirin sun hadar da guda uku a garin Hadejia da daya a Dutse da daya a Ringim da uku a Kazaure da kuma daya a Maigatari da daya a Babura.
- An yi bikin rantsar da Vladimir Putin a matsayin shugaban Rasha karo na biyar
- An ci gaba da ƙidayar kuri’u bayan kammala zaɓen shugaban kasa a jiya a ƙasar Chadi
- Gwamnan jihar Yobe ya jinjinawa sojojin Najeriya kan yadda suka fatattaki mayakan Boko Haram
- Jihar Borno ta yi asarar kusan kashi 53 cikin 100 na ma’aikatanta na kiwon lafiya sakamakon rikicin Boko Haram
- Najeriya za ta tsare kanta domin yaki da kasar Rasha
Dr. Nura Ibrahim yace kawo yanzu sun shigar da ma’aikatan jiha da kananan hukumomi da na sashen ilmi dubu 25 da 116 ne aka yiwa rijista kawo yanzu.
Yace a mako mai zuwa jirgin rijistar zai ziyarci kananan hukumomin Mallam Madori da Auyo da Kaugama.