Asusun kiwon lafiya na jihar Jigawa yace kawo yanzu asibitoci masu zaman kansu guda 10 ne suka nuna sha’awarsu ta shiga shirin asusun adashen gata na kiwon lafiya na jiha.
Sakataren zartarwa na asusun Dr Nura Ibrahim ya sanar da haka ga Radio Jigawa.
Yace daga cikin asibitocin masu zaman kansu da suka yi rijistar shiga shirin sun hadar da guda uku a garin Hadejia da daya a Dutse da daya a Ringim da uku a Kazaure da kuma daya a Maigatari da daya a Babura.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
Dr. Nura Ibrahim yace kawo yanzu sun shigar da ma’aikatan jiha da kananan hukumomi da na sashen ilmi dubu 25 da 116 ne aka yiwa rijista kawo yanzu.
Yace a mako mai zuwa jirgin rijistar zai ziyarci kananan hukumomin Mallam Madori da Auyo da Kaugama.