Jam’iyyar PDP ta yi watsi da kiran kara wa’adin zaben kananan hukumomi a Jigawa

Jam’iyyar PDP reshen jihar Jigawa ta yi watsi da kiran da majalisar ta bayarda shawarwari ga dukan jam’iyyu reshen jihar nan na a kara wa’adin shekara guda domin gudanar da zaben kananan hukumomi.

An zabi shugabannin kananan hukumomi 27 na yanzu da kansiloli 287 a watan Maris na 2021 na tsawon shekaru uku.

A wani taro da aka yi a Dutse, IPAC, ta ce karin wa’adin zai ba da damar shirya yadda ya kamata a gudanar da zaben kananan hukumomin.

Da yake zantawa da manema labarai, shugaban jam’iyyar PDP na karamar hukumar Dutse, Alhaji Sa’adu Barwa Dutse, ya ce wasu tsirarun mutane a IPAC ne kawai suke kokarin tilasta wa masu rinjaye ra’ayin. Barwa ya zargi shugabancin IPAC dayin aiki da jam’iyyar APC mai mulki domin yin tilasta bin ra’ayin dage zaben.

Comments (0)
Add Comment