Mai Martaba Sarkin Hadejia, Alhaji Dr Adamu Abubakar Maje CON, ya jaddada cikakken hadin kai da goyon bayan sarakuna wajen tabbatar da samun nasarar shirin yaki da bahaya a bainar jama’a a kowanne mataki.
Mai Martaba Sarki, ya bada wannan tabbaci ne a jiya lokacin da ya karbi wata tawaga ta kwamatin aiwatar da shirin a jihar nan, wadda kwamishinan ma’aikatar albarkatun ruwa na jiha Alhaji Ibrahim Garba Hannun Giwa ya ke jagoranta wadda suka ziyarci fadar sarkin.
- Burkina Faso ta dakatar da wasu kafafen watsa labarai da dama na Ƙasashen Yamma har sai baba ta gani
- Karyewar gada ta yi sanadiyyar mutuwar mutum 24 a lardin Guangdong na kudancin kasar China
- Isra’ila na dab da fara kai hare-hare birnin Rafah na kudancin Gaza ta ƙasa – Martin Griffiths
- Gwamnonin jahohin arewa sun bayyana damuwa bisa cigaba da karuwar rashin tsaro a shiyyar
- Gwamnatin Tarayya ta shirya tsaf domin bayar da cikakkiyar dama ga matatar man fetur ta Dangote
Mai Martaba Sarkin wanda shine shugaban majalisar sarakunan jihar Jigawa, ya umarci hakimai da dagatai da masu unguwanni dake masarautarsa da su fadakar da jama’a game da illolin bahaya a bainar jama’a. Tun da farko, kwamishina yace sun ziyarci fadar ne domin sanar da mai Martaba Sarki al’amuran da suka jibinci aiwatar da shirin yaki da bahaya a bainar jama`a, a kananan hukumomin Auyo da Kafin Hausa da kuma Birniwa.