Tsawa a jiya Laraba ta kashe jami’ai 3 na hukumar kiyaye hadura ta kasa, dake aiki da reshen hukumar na jihar Ogun.
Ance tsawa ta fada kan jami’an a ofishinsu dake tsohon toll gate a Ilese, yankin karamar hukumar Ijebu ta Arewa da Gabas, dake jihar.
- Akalla mutane 24 ne suka mutu sanadiyyar wani gini da ya ruguje a ƙasar Afrika ta Kudu
- Rundunar tsaro ta hadin gwiwa ta kubutar da wasu fasinjoji 17 da aka sace a jihar Katsina
- EFCC ta kama wasu mutane 26 da ake zargi da damfara ta intanet a jihar Ribas
- Wata Kungiya mai zaman kanta ta yi aikin jinya ga mata manoma 200 a jihar Jigawa
- Kotu ta hukunta Ramat Mba bisa laifin yin jabun sa hannun Marigayi Abba Kyari
- Asusun IMF ya gargadi gwamnatin tarayya da ta cire tallafin man fetur da wutar lantarki
An gano cewa lamarin ya auku da misalin karfe 10 na safe lokacin da jami’an hukumar ke shirin atisayen safiya.
Jami’ar ilimintar da jama’a ta hukumar kiyaye hadura, reshen jihar Ogun, Florence Okpe, ta tabbatar da aukuwar lamarin.
Okpe, sai dai, tace har yanzu ba a san musabbabin mutuwar
ba.