Kasar Jamus Ta Kawowa Nijeriya Agaji Don Yaki Da Korona

Jamus ta sanar da gudunmawar kudi euro miliyan 26, kwatankwacin Naira Biliyan 11 da miliyan 325 da dubu 630 da 732, domin agazawa Najeriya a yakin da take da cutar corona.

Ofishin jakadancin Jamus a Najeriya cikin wata sanarwa yace an bayar da gudunmawar domin nuna goyon baya da hadin kai ga Najeriya a lokacin annobar.

Sanarwar ta yi nuni da cewa kudaden zasu samar da ayyukan agaji a Arewa Maso Gabas, musamman a jihoshin Borno da Yobe da Adamawa.

Sanarwar ta yi bayanin cewa gwamnatin Jamus tana samar da tallafin kudade domin ayyukan agaji a Arewa maso Gabas na Najeriya da yankunan kan iyaka na Chadi da Nijar da Kamaru.

Ofishin jakadancin yayi bayanin cewa euro miliyan 8 zai tafi zuwa shirin abinci na majalisar dinkin duniya a Najeriya, euro miliyan 7 zai tafi zuwa kwamitin kasa da kasa na Red Cross a Najeriya, yayin da euro miliyan 5 zai je ga hukumar abinci da aikin gona ta majalisar dinkin duniya a Najeriya, da sauransu.

COVID - 19GermanyKORONANigeria
Comments (0)
Add Comment