Jamus ta sanar da gudunmawar kudi euro miliyan 26, kwatankwacin Naira Biliyan 11 da miliyan 325 da dubu 630 da 732, domin agazawa Najeriya a yakin da take da cutar corona.
Ofishin jakadancin Jamus a Najeriya cikin wata sanarwa yace an bayar da gudunmawar domin nuna goyon baya da hadin kai ga Najeriya a lokacin annobar.
Sanarwar ta yi nuni da cewa kudaden zasu samar da ayyukan agaji a Arewa Maso Gabas, musamman a jihoshin Borno da Yobe da Adamawa.
- Airtel ta dakatar da bayar da bashin kati da data a Najeriya
- ’Yan adawa ba su isa su razanar da ni ba – Tinubu
- Sojoji sun kama masu satar man fetur a Legas, sun kama mutum 14
- Talauci ya ragu daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto
- Bayan shekaru 12 da sace ɗaliban Chibok 272, har yanzu ba a san makomar 83 ba
Sanarwar ta yi bayanin cewa gwamnatin Jamus tana samar da tallafin kudade domin ayyukan agaji a Arewa maso Gabas na Najeriya da yankunan kan iyaka na Chadi da Nijar da Kamaru.
Ofishin jakadancin yayi bayanin cewa euro miliyan 8 zai tafi zuwa shirin abinci na majalisar dinkin duniya a Najeriya, euro miliyan 7 zai tafi zuwa kwamitin kasa da kasa na Red Cross a Najeriya, yayin da euro miliyan 5 zai je ga hukumar abinci da aikin gona ta majalisar dinkin duniya a Najeriya, da sauransu.