Jamus ta sanar da gudunmawar kudi euro miliyan 26, kwatankwacin Naira Biliyan 11 da miliyan 325 da dubu 630 da 732, domin agazawa Najeriya a yakin da take da cutar corona.
Ofishin jakadancin Jamus a Najeriya cikin wata sanarwa yace an bayar da gudunmawar domin nuna goyon baya da hadin kai ga Najeriya a lokacin annobar.
Sanarwar ta yi nuni da cewa kudaden zasu samar da ayyukan agaji a Arewa Maso Gabas, musamman a jihoshin Borno da Yobe da Adamawa.
- Akalla mutane 2,000 ne suka amfana tallafin Shinkafa daga AA Rano a karamar Hakumar Hadejia
- Kwamishinan ‘yan sandan Kano ya ziyarci kasuwar Kwalema, inda aka samu tashin gobara
- Gwamnatin jihar Jigawa ta tallafawa mata da rabon awaki 264 a karamar hakumar Birniwa.
- Kungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP sunyi alwashin kalubalantar matakin Tinubu kan jihar Rivers
- Za mu bi hanyoyin da doka ta tanada wurin dawo mana da haƙƙinmu – Fubara
Sanarwar ta yi bayanin cewa gwamnatin Jamus tana samar da tallafin kudade domin ayyukan agaji a Arewa maso Gabas na Najeriya da yankunan kan iyaka na Chadi da Nijar da Kamaru.
Ofishin jakadancin yayi bayanin cewa euro miliyan 8 zai tafi zuwa shirin abinci na majalisar dinkin duniya a Najeriya, euro miliyan 7 zai tafi zuwa kwamitin kasa da kasa na Red Cross a Najeriya, yayin da euro miliyan 5 zai je ga hukumar abinci da aikin gona ta majalisar dinkin duniya a Najeriya, da sauransu.