Hukumar abinci ta majalisar dinkin duniya ta ayyana cewa annobar corona zata iya jawo asarar guraben ayyukan yi miliyan 13 a Najeriya.
A cewar hukumar, Najeriya na bukatar agajin gaggawa na kudade domin bunkasa tattalin arzikin kasar, kasancewar miliyoyin yan kasarnan a halin yanzu suna fuskantar mummunar illar da kwayar cutar ta yiwa tattalin arziki.
- Airtel ta dakatar da bayar da bashin kati da data a Najeriya
- ’Yan adawa ba su isa su razanar da ni ba – Tinubu
- Sojoji sun kama masu satar man fetur a Legas, sun kama mutum 14
- Talauci ya ragu daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto
- Bayan shekaru 12 da sace ɗaliban Chibok 272, har yanzu ba a san makomar 83 ba
Babbar mai magana da yawun bakin hukumar, Elisabeth Baris ta fada cikin wata sanarwar da hukumar ta fitar cewa ana bukatar kudi sama da dala Miliyan 182 domin cigaban ayyukan ceton rayuwa a kasarnan wacce tafi kowacce yawan mutane a nahiyar Afirka, cikin watannin 6 masu zuwa.
Ta bayyana cewa sama da ‘yan kasarnan miliyan 3 da dubu 800, musamman masu kananan sana’o’i, zasu iya rasa ayyukan su, inda ta kara da cewa adadin zai iya karuwa zuwa miliyan 13 muddin dokar hana tafiye-tafiye ta cigaba da aiki tsawon lokaci.