Hukumar abinci ta majalisar dinkin duniya ta ayyana cewa annobar corona zata iya jawo asarar guraben ayyukan yi miliyan 13 a Najeriya.
A cewar hukumar, Najeriya na bukatar agajin gaggawa na kudade domin bunkasa tattalin arzikin kasar, kasancewar miliyoyin yan kasarnan a halin yanzu suna fuskantar mummunar illar da kwayar cutar ta yiwa tattalin arziki.
- Gwamnatin jihar Kano ta umarci lauyoyinta su yi nazarin umarnin kotun ɗaukaka ƙara
- An Kama Matar da Ta Kashe Kishiyarta da Ruwan Zafi A Jihar Jigawa
- Cutar sankarau na neman zama ruwan dare a jihar Bauchi
- Hukumar INEC ta biya diyya ga wani jami’inta da ya ji rauni a lokacin zaben 2023
- Gwamnan jihar Rivers ya sake rubuta wa majalisar jihar wasiƙar neman sake gabatar da kasafin kuɗi
Babbar mai magana da yawun bakin hukumar, Elisabeth Baris ta fada cikin wata sanarwar da hukumar ta fitar cewa ana bukatar kudi sama da dala Miliyan 182 domin cigaban ayyukan ceton rayuwa a kasarnan wacce tafi kowacce yawan mutane a nahiyar Afirka, cikin watannin 6 masu zuwa.
Ta bayyana cewa sama da ‘yan kasarnan miliyan 3 da dubu 800, musamman masu kananan sana’o’i, zasu iya rasa ayyukan su, inda ta kara da cewa adadin zai iya karuwa zuwa miliyan 13 muddin dokar hana tafiye-tafiye ta cigaba da aiki tsawon lokaci.