Da Matsala: Mutane Miliyan 13 Zasu Rasa Aikinsu A Nijeriya – Rahoto

0 112

Hukumar abinci ta majalisar dinkin duniya ta ayyana cewa annobar corona zata iya jawo asarar guraben ayyukan yi miliyan 13 a Najeriya.

A cewar hukumar, Najeriya na bukatar agajin gaggawa na kudade domin bunkasa tattalin arzikin kasar, kasancewar miliyoyin yan kasarnan a halin yanzu suna fuskantar mummunar illar da kwayar cutar ta yiwa tattalin arziki.

Babbar mai magana da yawun bakin hukumar, Elisabeth Baris ta fada cikin wata sanarwar da hukumar ta fitar cewa ana bukatar kudi sama da dala Miliyan 182 domin cigaban ayyukan ceton rayuwa a kasarnan wacce tafi kowacce yawan mutane a nahiyar Afirka, cikin watannin 6 masu zuwa.

Ta bayyana cewa sama da ‘yan kasarnan miliyan 3 da dubu 800, musamman masu kananan sana’o’i, zasu iya rasa ayyukan su, inda ta kara da cewa adadin zai iya karuwa zuwa miliyan 13 muddin dokar hana tafiye-tafiye ta cigaba da aiki tsawon lokaci.

Leave a Reply

%d bloggers like this: