Rundunar ‘yansandan jihar Kano tace ta kama wani mutum bisa zargin yiwa mata sama da 40 fyade a jihar.
Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar DSP Abdullahi Haruna ya rabawa manema labarai a Kano.
Yace yansanda sun kama Muhammad Alfa mai shekaru 32 a duniya a Kwanar Dangora, kusa da birnin Kano.
- Sanata Shehu Buba zai horas da matasa 250 kan sana’ar gyaran takalma a jihar Bauchi
- Cibiyoyin kula da lafiyar kafafu da hannaye a Najeriya ta bude sabon ofishi a Kano
- Gwamnan Namadi ya amince da Mai Martaba Sarkin Kazaure a matsayin Amirul Hajj na jihar Jigawa
- Dalibai 41,000 da ba su kai shekara 16 ba sun yi rajistar JAMB ta shekarar 2025
- Za a fara gudanar da jarrabawar WAEC da NECO ta hanyar na’ura wato CBT
Ya kara da cewa yayin bincike, mutumin ya furta cewa ya yiwa sama da mata 40 fyade a shekara guda, cikinsu har da yara, da matan aure, har da wata tsohuwar ‘yar shekaru 80.
A cewarsa, an kama mai laifin lokacin da yake kokarin yiwa wata matar aure fyade a gidanta.
Abdullahi Haruna yace jama’a sun yi farin ciki bayan samun labarin cewa ‘yansanda sun kama mutumin.