Rundunar ‘yansandan jihar Kano tace ta kama wani mutum bisa zargin yiwa mata sama da 40 fyade a jihar.
Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar DSP Abdullahi Haruna ya rabawa manema labarai a Kano.
Yace yansanda sun kama Muhammad Alfa mai shekaru 32 a duniya a Kwanar Dangora, kusa da birnin Kano.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
Ya kara da cewa yayin bincike, mutumin ya furta cewa ya yiwa sama da mata 40 fyade a shekara guda, cikinsu har da yara, da matan aure, har da wata tsohuwar ‘yar shekaru 80.
A cewarsa, an kama mai laifin lokacin da yake kokarin yiwa wata matar aure fyade a gidanta.
Abdullahi Haruna yace jama’a sun yi farin ciki bayan samun labarin cewa ‘yansanda sun kama mutumin.