Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka

Ƙasar Jamus ta ƙulla yarjejeniya da Najeriya na maido da wasu dubban kayayyakin tarihi da aka wawushe a zamanin mulkin mallaka.

An miƙa wasu biyu daga cikin kayayyakin tarihin a wani biki a Berlin.

A shekarar 1897 ne sojojin Birtaniya suka sace tagulla daga Masarautar Benin, wato jihar Edo ta Najeriya a yau.

Daga nan aka yi gwanjon su zuwa gidajen tarihi na Turai da Arewacin Amurka, da kuma Jamus, ta biyu da ta fi karɓar kayayyakin a duniya bayan gidan kayan tarihi na Biritaniya.

Jakadan Najeriya a Jamus Yusuf Maitama Tugga ya shaida wa BBC cewa za a iya dawo wa Najeriya da kayayyakin nan da mako mai zuwa.Article

Comments (0)
Add Comment