Kimanin mutane 2 ne suka mutu biyo bayan wani haɗarin mota da ya afku a jihar Bauchi

Kimanin mutane 2 ne suka mutu a jiya, biyo bayan wani hadarin mota da ya afku a Jihar Bauchi.

Kwamandan Hukumar Kiyaye Afkuwar Hadura ta Kasa reshen Jihar Bauchi Mr. Yusuf Abdullahi, shine ya bayyana hakan ga manema labarai, inda ya ce mutane 6 ne suka samu raunika a lokacin hadarin.

Haka kuma ya ce hadarin ya shafi wata motar haya guda 1 a kasuwar Durum wanda take kan hanyar Bauchi zuwa Kano.

Kwamandan ya ce mutane 8 ne hadarin ya shafa wanda suka hada da Maza 5 da Mata 2 da kuma karamin Yaro.

A cewarsa, hadarin ya faru ne saboda gudun wuce sa’a a tsakanin motocin hayar, wanda hakan ke haifar da asarar rayuka.

Kazalika, ya ce an kai Direban Motar zuwa Asibitin Koyarwa na Abubakar Tafawa Balewa na Jihar Bauchi.

Comments (0)
Add Comment