Shugaban hukumar shige da fice ta kasa Muhammad Babandede yayi zargin cewa akwai almundahana a wata kwangilar katin shaidar zama a kasa domin kwararru ‘yan kasashen waje, wacce aka sanyawa hannu tsakanin ma’aikatar cikin gida da wani kamfanin fasaha a shekarar 2007.
Kamfanin abokin hulda ne na hukumar shige da fice ta kasa, wajen samar da katin shaidar zama a kasa domin kwararru ‘yan kasashen waje.
- Sarki Charles zai koma aiki makon gobe
- Amurka ta bayar da bayanin tallafin soji na $6Bn da ta bai wa Ukriane
- Japan za ta taimakawa ƙananan ma’aikata a Najeriya domin samar da shinkafa
- Gwamnatin Jigawa ta jadadda kudirinta na daukar kwararan matakai na rage talauci a jihar
- An kama haramtattun nakiyoyi 6,240 a hanyar Yauri zuwa Jega da ke Jihar Kebbi
Katin shaidar tilas ne ga kwararru ‘yan kasashen waje a Najeriya. Yana basu daman su zauna tare da yin aiki a kasarnan, kuma ana iya sabunta shi kowace shekara, ko bayan shekara biyu, dogaro da shekarun aikin da aka sanya masa.
Zarge-zargen sun zo kimanin watanni goma sha takwas bayan ma’aikatar cikin gida, karkashin tsohon minista Abdurrahman Dambazau, ta kara farashin katin daga Dala dubu daya zuwa Dala dubu biyu a ranar goma sha uku ga watan Disambar 2018, biyo bayan bukatar hakan da kamfanin ya nema.