A karon farko tun watan Afrilu, yawan wadanda suka kamu da corona a Najeriya cikin rana guda yayi kasa da 100.
Hukumar dakile yaduwar cututtuka ta kasa NCDC ta tabbatar da samun sabbin mutane 79 a jiyar Lahadi da dare, adadi mafi karanci a cikin kusan watanni biyar.
An samu sabbin mutanen a jihoshi 12 da babban birnin tarayya.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
An kuma samu rahoton sabbin mutane 4 da cutar ta hallaka a jiyan, inda jumillar wadanda cutar ta kashe ya kai dubu 1 da 82.
Kazalika, da mutane 64 da suka warke kuma aka sallamesu a jiya, an samu rahoton karancin wadanda suka warke daga cutar a rana guda tun ranar 21 ga watan Mayu.
Daga cikin mutane dubu 56 da 256 da yanzu aka tabbatar sun kamu da cutar corona a jihoshi 36 da babban birnin tarayya, mutane dubu 44 da 152 sun warke.