Ofishin hukumar wayar da kan jama`a ta kasa a jihar Jigawa ta gudanar da taron gangami a karamar hukumar Malam-Madori domin fadakar da al`umma illolin da cutar Korona virus ta haifar a fannonin tsaro da zamantakewa.
A jawabin da ya gabatar Daraktan hukumar na jiha, Malam Shu`aibu Karamba Haruna yayi dogon bayani akan matakan da ya kamata a dauka domin kare yaduwar cutar Covid-19.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
Haka kuma ya bukaci jama`a su tabbatar suna bin dukkanin ka`idojin da hukumomin lafiya suka tanada domin kare yaduwar cutar.
A lokacin gangamin wani jami`in hukumar wayar da kan jama`a ta kasa, Malam Tijjani ya gabatar da makala mai taken tasirin cutar Covid-19 akan tattalin arziki da karuwar aikata laifuka da kuma rigingimu tsakanin Fulani da manoma.
A nasa jawabin shugaban karamar hukumar Malam-Madori wanda ya sami wakilcin Daraktan tsare-tsare na yankin, Malam Lawan Bawa ya jaddada kudurin karamar hukumar na hada kai da hukumar domin cimma biyan bukata.
Mahalarta taron sun hadar da yan`kungiyoyi masu zaman kansu da kungiyar Miyetti Allah da jami`an hukumar kiyaye haddura ta kada limamai da masu ruwa da tsaki.