Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Juma’a 12 ga watan Yuni a matsayin ranar hutun ranar demokradiyya ta bana.
Ministan cikin gida, Rauf Aregbesola, ya sanar da hakan cikin wata sanarwa a madadin gwamnatin tarayya.
Sanarwar wacce ke dauke da sa hannun babban sakataren ma’aikatar harkokin cikin gida, Georgina Ehuriah, ta jiyo Aregbesola na taya ‘yan Najeriya murnar dorewar mulkin demokradiyya a kasarnan.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
Ministan ya kuma yi kira ga ‘yan Najeriya da su cigaba da godewa kokarin da aka yi wajen dawo da mulkin demokradiyya.
Ya tabbatarwa da ‘yan Najeriya jajircewar gwamnatin tarayya wajen yaki da annobar corona tare da hadin kan dukkan ‘yan Najeriya.