Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Juma’a 12 ga watan Yuni a matsayin ranar hutun ranar demokradiyya ta bana.
Ministan cikin gida, Rauf Aregbesola, ya sanar da hakan cikin wata sanarwa a madadin gwamnatin tarayya.
Sanarwar wacce ke dauke da sa hannun babban sakataren ma’aikatar harkokin cikin gida, Georgina Ehuriah, ta jiyo Aregbesola na taya ‘yan Najeriya murnar dorewar mulkin demokradiyya a kasarnan.
- Gwamnatin Jigawa zata cigaba da tallafawa Jami’ar Fasaha ta gwamnatin tarayya dake garin Babura
- Aƙalla mutum 42 ne suka mutu sakamakon ƙyanda a jihar Adamawa
- Gwamnan Jihar Gombe ya yi kira ga sabbin zababbun shugabannin kananan hukumomi da su yi aiki tukuru
- Gwamna Dikko Radda ya kare ziyarar da gwamnonin Arewa suka kai kasar Amurka
- Kasar Turkiyya ta dakatar da duk wata hulɗar kasuwanci da Isra’ila
Ministan ya kuma yi kira ga ‘yan Najeriya da su cigaba da godewa kokarin da aka yi wajen dawo da mulkin demokradiyya.
Ya tabbatarwa da ‘yan Najeriya jajircewar gwamnatin tarayya wajen yaki da annobar corona tare da hadin kan dukkan ‘yan Najeriya.