Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Juma’a 12 ga watan Yuni a matsayin ranar hutun ranar demokradiyya ta bana.
Ministan cikin gida, Rauf Aregbesola, ya sanar da hakan cikin wata sanarwa a madadin gwamnatin tarayya.

Sanarwar wacce ke dauke da sa hannun babban sakataren ma’aikatar harkokin cikin gida, Georgina Ehuriah, ta jiyo Aregbesola na taya ‘yan Najeriya murnar dorewar mulkin demokradiyya a kasarnan.
- Tinubu ya amince da yin sabbin nade-nade guda hudu
- Ban san ko zan tsaya takarar shugabancin kasa a shekarar 2027 ba – Atiku
- Tinubu ya taya Goodluck Jonathan murna kan lashe kyautar “Sunhak Peace Founders Award” na shekarar 2025
- Masu haƙar kabari sun koka kan ƙarancin alawus ɗin da ake ba su na ₦3,000 a wata
- Waɗanda suka turo ƙorafin yi wa Natasha kiranye ba su saka adireshinsu ba
Ministan ya kuma yi kira ga ‘yan Najeriya da su cigaba da godewa kokarin da aka yi wajen dawo da mulkin demokradiyya.
Ya tabbatarwa da ‘yan Najeriya jajircewar gwamnatin tarayya wajen yaki da annobar corona tare da hadin kan dukkan ‘yan Najeriya.