Ranar Juma’a 12 ga watan Yuni ta zamo ranar hutun demokradiyya ta bana

0 102

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Juma’a 12 ga watan Yuni a matsayin ranar hutun ranar demokradiyya ta bana.

Ministan cikin gida, Rauf Aregbesola, ya sanar da hakan cikin wata sanarwa a madadin gwamnatin tarayya.

Sanarwar wacce ke dauke da sa hannun babban sakataren ma’aikatar harkokin cikin gida, Georgina Ehuriah, ta jiyo Aregbesola na taya ‘yan Najeriya murnar dorewar mulkin demokradiyya a kasarnan.

Ministan ya kuma yi kira ga ‘yan Najeriya da su cigaba da godewa kokarin da aka yi wajen dawo da mulkin demokradiyya.

Ya tabbatarwa da ‘yan Najeriya jajircewar gwamnatin tarayya wajen yaki da annobar corona tare da hadin kan dukkan ‘yan Najeriya.

Leave a Reply

%d bloggers like this: