Sanata mai wakiltar Jigawa ta Arewa maso Gabas,Brr. Ibrahim Hassan Hadejia ya bada gudunmawar takunkumin rufe hanci da baki guda dubu goma da dari shida da talatin ga makarantu domin rabawa daliban mazabarsa.
Wakilin Sanatan, Muhammad Lawan wanda ya mika gudunmawar kayayyakin yace hakan zai taimaka wajen marawa kudirin gwamnati baya na yaki da yaduwar cutar corona.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
Ya kuma bukaci malamai da dalibai dasu yi cikakken amfani da shi wajen kare kai daga kamuwa daga cutar inda kuma ya yabawa ma’aikatar ilmi bisa tsare-tsaren da tayi na samun nasarar rubuta jarabawar karshen ga dalibai.
Kazalika, Sanata Ibrahim Hassan Hadejia ya bada gudunmawar kayayyakin bada horo ga cibiyar rubuta jarabawar kammala sakandare ta NECO dake makarantar sakandaren Famfo Goma.