Sanata mai wakiltar Jigawa ta Arewa maso Gabas,Brr. Ibrahim Hassan Hadejia ya bada gudunmawar takunkumin rufe hanci da baki guda dubu goma da dari shida da talatin ga makarantu domin rabawa daliban mazabarsa.
Wakilin Sanatan, Muhammad Lawan wanda ya mika gudunmawar kayayyakin yace hakan zai taimaka wajen marawa kudirin gwamnati baya na yaki da yaduwar cutar corona.
- Gwamnatin Jigawa zata cigaba da tallafawa Jami’ar Fasaha ta gwamnatin tarayya dake garin Babura
- Aƙalla mutum 42 ne suka mutu sakamakon ƙyanda a jihar Adamawa
- Gwamnan Jihar Gombe ya yi kira ga sabbin zababbun shugabannin kananan hukumomi da su yi aiki tukuru
- Gwamna Dikko Radda ya kare ziyarar da gwamnonin Arewa suka kai kasar Amurka
- Kasar Turkiyya ta dakatar da duk wata hulɗar kasuwanci da Isra’ila
Ya kuma bukaci malamai da dalibai dasu yi cikakken amfani da shi wajen kare kai daga kamuwa daga cutar inda kuma ya yabawa ma’aikatar ilmi bisa tsare-tsaren da tayi na samun nasarar rubuta jarabawar karshen ga dalibai.
Kazalika, Sanata Ibrahim Hassan Hadejia ya bada gudunmawar kayayyakin bada horo ga cibiyar rubuta jarabawar kammala sakandare ta NECO dake makarantar sakandaren Famfo Goma.