Gwamnan jihar Jigawa Muhammadu Badaru Abubakar yayi tsinkayen cewa shirin tallafawa jama’a na Gwamnatin Buhari, shine wanda yafi kowanne a duniya.
Gwamnan ya sanar da haka a garin Gagarawa wajen kaddamar da shirin a karin kananan hukumomi goma sha takwas na jihar.
Yace wadanda ke sukar Gwamnati, masu fada aji ne sosai, wadanda basu da matsala idan komai ya lalace, domin su samu damar cigaba da wadaka da dukiyar jama’a ido rufe.
- Za’a farfado da ayyukan kungiyoyin taimakon kai da kai a jihar Jigawa
- Hukumar STOWA zata fara rangadi shiyoyin hukumar guda bakwai daga mako mai zuwa
- ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da dalibai mata biyu na kwalejin kimiyya da fasaha da ke Tsafe
- Hukumar kula da filayen jiragen sama ta Najeriya ta fara sayar da takardar sheda na shekarar 2024
- Najeriya kasa ce mai aminci ga masu saka hannun jari – Bola Tinubu
Gwamnan yace jihar ce kan gaba wajen yawan mutanen da ke cin gajiyar shirin, inda aka biya naira biliyan tara da miliyan saba’in da hudu ga mutane dubu ashirin da shida da dari bakwai da talatin da hudu, tsakanin watan Augustan 2017 zuwa Aprilun bana.
Yayi bayanin cewa an kaddamar ne domin mutane dubu ashirin da shida da dari bakwai da talatin da hudu, yayin da aka zabi karin mutane dubu talatin da daya da dari tara da arba’in da tara domin biyansu kudaden wata-wata a karkashin shirin.