

Gwamnan jihar Jigawa Muhammadu Badaru Abubakar yayi tsinkayen cewa shirin tallafawa jama’a na Gwamnatin Buhari, shine wanda yafi kowanne a duniya.
Gwamnan ya sanar da haka a garin Gagarawa wajen kaddamar da shirin a karin kananan hukumomi goma sha takwas na jihar.
Yace wadanda ke sukar Gwamnati, masu fada aji ne sosai, wadanda basu da matsala idan komai ya lalace, domin su samu damar cigaba da wadaka da dukiyar jama’a ido rufe.
- Tarihin Gamuwa 10 Tsakanin Kano Pillars VS Eyimba Da Kuma Wasan Yau
- Abubuwa 5 da suka zama wajibi lokacin sanyi
- An ƙaddamar da kudin kariya ga ƴan jarida da masu fafutukar ƴancin amfani da yanar gizo
- Yadda ake duba suna don zama ma’aikacin damara na 2020 a Nijeria
- Me Ƙungiyar Izala ta ce kan matsalolin tsaro a Najeriya?
Gwamnan yace jihar ce kan gaba wajen yawan mutanen da ke cin gajiyar shirin, inda aka biya naira biliyan tara da miliyan saba’in da hudu ga mutane dubu ashirin da shida da dari bakwai da talatin da hudu, tsakanin watan Augustan 2017 zuwa Aprilun bana.
Yayi bayanin cewa an kaddamar ne domin mutane dubu ashirin da shida da dari bakwai da talatin da hudu, yayin da aka zabi karin mutane dubu talatin da daya da dari tara da arba’in da tara domin biyansu kudaden wata-wata a karkashin shirin.