Asusun Tallafawa Jami’an Tsaro Na Musamman Zai Taimaka Wajen Dakile Matsalar Tsaro – Tambuwal

0 113

Gwamnan Jihar Sokoto Aminu Waziri Tambuwal, yayi kira da a samar da Asusun Tsaro na Musamman ga Sojoji da Yan sanda da sauran Hukumomin tsaro wanda hakan zai basu damar Mallakar Sabbin Makamai.

A cewarsa Matsalolin da Jami’an suke samu nada alaka da karancin Makamai da kuma sauran Matsaloli na bukatunsu.

Gwamna Tambuwal ya bayar da shawararar ne a lokacin da ya kaiwa Gwamnan Jihar Zamfara Dr Bello Matawallen Maradun, da Kuma Sansanin Soji ta 4 a Faskari ta Jihar Katsina ziyara.

Haka kuma ya dora Alhakin Matsalar tsaro da ake samu a kasar nan akan Yan Siyasa.

Leave a Reply

%d bloggers like this: