Gwamnan Jihar Sokoto Aminu Waziri Tambuwal, yayi kira da a samar da Asusun Tsaro na Musamman ga Sojoji da Yan sanda da sauran Hukumomin tsaro wanda hakan zai basu damar Mallakar Sabbin Makamai.
A cewarsa Matsalolin da Jami’an suke samu nada alaka da karancin Makamai da kuma sauran Matsaloli na bukatunsu.
![](https://i0.wp.com/www.sawabafm.com/wp-content/uploads/2020/07/security.jpg?resize=300%2C168&ssl=1)
Gwamna Tambuwal ya bayar da shawararar ne a lokacin da ya kaiwa Gwamnan Jihar Zamfara Dr Bello Matawallen Maradun, da Kuma Sansanin Soji ta 4 a Faskari ta Jihar Katsina ziyara.
Haka kuma ya dora Alhakin Matsalar tsaro da ake samu a kasar nan akan Yan Siyasa.