

Tsohon shugaban kasa Olusegun Obansanjo yayi kira ga matasan Afirka da su kawar da dattawa daga shugabanci.
Obasanjo ya bukaci matasan da su tsunduma a harkokin jam’iyyun siyasa domin kwace madafun iko daga hannunsu.
Tsohon shugaban kasar ya fadi haka a jiya lokacin da yake gabatar da jawabi a wajen wata tattaunawa ta bidiyon kai tsaye, domin tunawa da ranar matasa ta duniya ta bana.
- Tarihin Gamuwa 10 Tsakanin Kano Pillars VS Eyimba Da Kuma Wasan Yau
- Abubuwa 5 da suka zama wajibi lokacin sanyi
- An ƙaddamar da kudin kariya ga ƴan jarida da masu fafutukar ƴancin amfani da yanar gizo
- Yadda ake duba suna don zama ma’aikacin damara na 2020 a Nijeria
- Me Ƙungiyar Izala ta ce kan matsalolin tsaro a Najeriya?
Cibiyar cigaban matasa, wacce bangare ne na dakin karatun shugaban kasa na Olusegen Obansanjo dake Abekutan jihar Ogun, ta shirya tattaunawar.
An zabo mahalarta daga Najeriya da Mali da Amurka da Ghana da Kenya da Afirka ta Kudu.
A cewarsa, muddin ba dattawa aka kora daga siyasa ba, zasu cigaba da rike mukamai, suna barin matasa a iska.