Tsohon shugaban kasa Olusegun Obansanjo yayi kira ga matasan Afirka da su kawar da dattawa daga shugabanci.
Obasanjo ya bukaci matasan da su tsunduma a harkokin jam’iyyun siyasa domin kwace madafun iko daga hannunsu.
Tsohon shugaban kasar ya fadi haka a jiya lokacin da yake gabatar da jawabi a wajen wata tattaunawa ta bidiyon kai tsaye, domin tunawa da ranar matasa ta duniya ta bana.
- Airtel ta dakatar da bayar da bashin kati da data a Najeriya
- ’Yan adawa ba su isa su razanar da ni ba – Tinubu
- Sojoji sun kama masu satar man fetur a Legas, sun kama mutum 14
- Talauci ya ragu daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto
- Bayan shekaru 12 da sace ɗaliban Chibok 272, har yanzu ba a san makomar 83 ba
Cibiyar cigaban matasa, wacce bangare ne na dakin karatun shugaban kasa na Olusegen Obansanjo dake Abekutan jihar Ogun, ta shirya tattaunawar.
An zabo mahalarta daga Najeriya da Mali da Amurka da Ghana da Kenya da Afirka ta Kudu.
A cewarsa, muddin ba dattawa aka kora daga siyasa ba, zasu cigaba da rike mukamai, suna barin matasa a iska.