Kimanin Masu karamin karfi dubu daya da dari biyar da talatin da hudu ne da aka zabo daga garuruwa goma sha biyar a yankin karamar hukumar Birniwa zasu amfana da tallafin naira dubu biyar-biyar karkashin shirin rage radadin talauci na kasa.
Manajan ofishin shirin biyan kudade na jiha, Kabiru Yahaya Abdulkadir, ya bayyana haka lokacin raba koren katin karbar tallafin a sakatariyar karamar hukumar Birniwa.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
A nasa jawabin shugaban karamar hukumar wanda ya samu wakilcin mataimakinsa Alhaji Umar Baffa ya yabawa gwamnatin shugaban kasa Muhammad Buhari bisa bada tallafi ga masu karamin karfi.
Tunda farko a jawabinsa jami’in kula da shirin na karamar hukumar, Shehu Baba Birniwa ya ce wannan shi ne karon farko da al’ummar karamar hukumar zasu ci gajiyar shirin.