Kimanin Masu karamin karfi dubu daya da dari biyar da talatin da hudu ne da aka zabo daga garuruwa goma sha biyar a yankin karamar hukumar Birniwa zasu amfana da tallafin naira dubu biyar-biyar karkashin shirin rage radadin talauci na kasa.
Manajan ofishin shirin biyan kudade na jiha, Kabiru Yahaya Abdulkadir, ya bayyana haka lokacin raba koren katin karbar tallafin a sakatariyar karamar hukumar Birniwa.
- Ina alfahari da samun dimbin goyon bayan da ake bukata domin zama ‘yartakara – Kamala Harris
- An bukaci mazauna jihar Jigawa da su kula da matakan kariya domin dakile ambaliyar ruwa
- Ƙasashe 58 sun goyi bayan Ngozi Okonjo-Iweala ta yi tazarce a Shugabar Kungiyar Cinikayya ta Duniya
- Kungiyar Kwadago ta yi gargadi kan yunkurin dakushe zanga-zangar da ake shirin yi a fadin kasar
- Gwamnatin Tarayya ta gabatar da buƙatar ƙarin Naira tiriliyan 6.2 akan kasafin kuɗin bana
A nasa jawabin shugaban karamar hukumar wanda ya samu wakilcin mataimakinsa Alhaji Umar Baffa ya yabawa gwamnatin shugaban kasa Muhammad Buhari bisa bada tallafi ga masu karamin karfi.
Tunda farko a jawabinsa jami’in kula da shirin na karamar hukumar, Shehu Baba Birniwa ya ce wannan shi ne karon farko da al’ummar karamar hukumar zasu ci gajiyar shirin.