Akalla mamata dari uku da goma sha biyu aka samu cikin yan fanshon kananan hukumomi, wadanda ake biya fansho a jihar Bauchi.
Kazalika, an gano mamata tara da ake biya fansho a gwamnatin jihar.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
Mai bawa gwamnan Bauchi shawara ta musamman kan harkokin aikin gwamnati, Abdon Gin, wanda ya sanar da haka a wajen taron manema labarai jiya a Bauchi, yace Gwamnatin jihar ta adana kudi sama da naira miliyan casa’in da daya da dubu dari hudu da hudu, da dari biyu da casa’in da shida da kwabo goma sha tara bayan gano mamatan.
Yace wani kwamitine da gwamnan jihar ya kafa domin tantance ma’aikata da basu da shaidar banki, ya bankado badakalar.