Wasu alkaluma da babban bankin kasa CBN ya fitar na nuni da cewa, asusun kasar wajen Najariya ya fado da kimanin dalar Amurka miliyan 544, daga jimillar dala biliyan 36 da miliyan 17 a 1 ga watan yuli, zuwa jimillar dala biliyan 35 da miliyan 62 a ranar 13 ga watan Agustan da muke ciki.
A wani zama da kwamatin tsare tsaren kudade ya gudanar, babban bankin ya nanata cewa, faduwar farashin mai ya shafi harkokin musayar kudaden kasarnan.
- ‘Yan bindiga sun kashe babban limamin masallacin Juma’a na kauyen Keita
- Gobara ta ƙone motoci da rumfunan katako takwas da kuma kayan aikin kafinta ƙurmus
- Kwamitin Masallacin Dutse ya raba buhunan Shinkafa buhu 30,000 ga zawarawa da sauran marasa galihu
- Kwamandojin Boko Haram biyu sun mika wuya ga sojojin rundunar hadin gwiwa ta MNJTF
- Dan takarar jam’iyyar adawa Bassirou Diomaye Faye ne ke kan gaba a zaben shugaban kasar Senegal
A cewar kwamatin tsare tsaren, matakan kulle da na tsagaita tafiye tafiye, da aka sanya sabida Corona, zai cigaba da yin tasiri wajen nukusa tattalin arzikin kasarnan.
A zaman karshe da kwamatin yayi, gwamnan babban bankin Mr Godwin Emefiele, ya bukaci gwamnati da ta dauki matakan rage dogaro da mai, ta hanyar fadada harkokin tattalin arziki da tattara kudaden haraji.