Majalisar wakilai ta kasa zata gana da ministoci da manyan jami’an gwamnati, domin amsa tambayoyi kan kudaden bashi da kasarnan ke karbowa daga ketare, musamman China.
Kwamatin majalisar na yarjejeniya, yayi kiranye ga ministar kudi, kasafi da tsare tsare, Zainab Ahmad, ministan Sadarwa da cigaban tattalin arziki ta yanar gizo, Dr. Isah Ali Pantami, sannan ministan wuta Sale Mamman, da ministan sufuri Rotimi Amaechi da kuma darakta janar ta ofishin dake kula da basuka, Patience Oniha da dai sauransu.
- An yi bikin rantsar da Vladimir Putin a matsayin shugaban Rasha karo na biyar
- An ci gaba da ƙidayar kuri’u bayan kammala zaɓen shugaban kasa a jiya a ƙasar Chadi
- Gwamnan jihar Yobe ya jinjinawa sojojin Najeriya kan yadda suka fatattaki mayakan Boko Haram
- Jihar Borno ta yi asarar kusan kashi 53 cikin 100 na ma’aikatanta na kiwon lafiya sakamakon rikicin Boko Haram
- Najeriya za ta tsare kanta domin yaki da kasar Rasha
Shugaban kwamatin Mr Nicolas Ossai, ya shaidawa manema labarai cewa, wadanda aka aikewa da kiranyen, ana sa ran su bayyana gaban kwamatin a yau Litinin.
Tun dai a ranar 28 ga watan yulin da ya gabata ne, kwamatin ya soma bincike kan kudaden bashi da kasarnan ke ciyowa, wanda ta fara da bashin dala miliyan 500 da aka karbo daga China, domin aikin titin jirgin kasa.
Yan majalisa dai sun bara kan yarjejeniyar bashi da kasarnan ta rattaba hannu da China a kai, wanda sukace tamkar mika wuya ne ga kasar idan aka gaza biya.