Kungiyar yan achaba ta jihar Kebbi ta nemi kariyar jami’an tsaro bayan barayi sun kashe yayan kungiyar hudu a jihar.
Shugaban kungiyar, Nafi’u Zaki, yayi kiran yayin wata ganawa da kamfanin dillancin labarai na kasa a Birnin Kebbi.
Nafi’u Zaki yace an kashe yayan kungiyar hudu a karamar hukumar Birnin Kebbi ta jihar.
- Sarki Charles zai koma aiki makon gobe
- Amurka ta bayar da bayanin tallafin soji na $6Bn da ta bai wa Ukriane
- Japan za ta taimakawa ƙananan ma’aikata a Najeriya domin samar da shinkafa
- Gwamnatin Jigawa ta jadadda kudirinta na daukar kwararan matakai na rage talauci a jihar
- An kama haramtattun nakiyoyi 6,240 a hanyar Yauri zuwa Jega da ke Jihar Kebbi
Yace ana tsayar da mutanensu a dake su, wasu lokutan a yanke da wuka a kashe su.
Yace kafin yan kwanakinnan, kungiyar bata da rahoton wani dan kungiyar da aka kashe a kokarin kwace masa babur.
Nafi’u Zaki yace kungiyar tana da mambobi wadanda suka yi rijista su dubu talatin da bakwai, inda ya kara da cewa dayawa daga cikinsu sun fito daga kauyuka da jihoshi makota.