Kungiyar yan achaba ta jihar Kebbi ta nemi kariyar jami’an tsaro bayan barayi sun kashe yayan kungiyar hudu a jihar.
Shugaban kungiyar, Nafi’u Zaki, yayi kiran yayin wata ganawa da kamfanin dillancin labarai na kasa a Birnin Kebbi.
Nafi’u Zaki yace an kashe yayan kungiyar hudu a karamar hukumar Birnin Kebbi ta jihar.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
Yace ana tsayar da mutanensu a dake su, wasu lokutan a yanke da wuka a kashe su.
Yace kafin yan kwanakinnan, kungiyar bata da rahoton wani dan kungiyar da aka kashe a kokarin kwace masa babur.
Nafi’u Zaki yace kungiyar tana da mambobi wadanda suka yi rijista su dubu talatin da bakwai, inda ya kara da cewa dayawa daga cikinsu sun fito daga kauyuka da jihoshi makota.