Kungiyar yan achaba ta jihar Kebbi ta nemi kariyar jami’an tsaro bayan barayi sun kashe yayan kungiyar hudu a jihar.
Shugaban kungiyar, Nafi’u Zaki, yayi kiran yayin wata ganawa da kamfanin dillancin labarai na kasa a Birnin Kebbi.
Nafi’u Zaki yace an kashe yayan kungiyar hudu a karamar hukumar Birnin Kebbi ta jihar.
- Airtel ta dakatar da bayar da bashin kati da data a Najeriya
- ’Yan adawa ba su isa su razanar da ni ba – Tinubu
- Sojoji sun kama masu satar man fetur a Legas, sun kama mutum 14
- Talauci ya ragu daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto
- Bayan shekaru 12 da sace ɗaliban Chibok 272, har yanzu ba a san makomar 83 ba
Yace ana tsayar da mutanensu a dake su, wasu lokutan a yanke da wuka a kashe su.
Yace kafin yan kwanakinnan, kungiyar bata da rahoton wani dan kungiyar da aka kashe a kokarin kwace masa babur.
Nafi’u Zaki yace kungiyar tana da mambobi wadanda suka yi rijista su dubu talatin da bakwai, inda ya kara da cewa dayawa daga cikinsu sun fito daga kauyuka da jihoshi makota.