Rundunar yansandan jihar Jigawa ta kame mutane 20 da take zargi da aikata laifuka daban-daban da suka hada da fashi da makami, garkuwa da mutane da kisan kai, inda ta kwato kayan sata daga hannunsu da kuma makamai.
Kwamishinan yansanda na jiha, Usman Sule Gomna, ya sanar da haka a taron manema labarai a Dutse.
Kwamishinan ya bayyana cewa tawagar yansanda ta musamman masu yaki da fashi da makami sun kai farmaki kan wasu maboyar ‘yan fashi a yankin karamar hukumar Ringim inda suka damke wasu daga cikin ‘yan fashin.
- Airtel ta dakatar da bayar da bashin kati da data a Najeriya
- ’Yan adawa ba su isa su razanar da ni ba – Tinubu
- Sojoji sun kama masu satar man fetur a Legas, sun kama mutum 14
- Talauci ya ragu daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto
- Bayan shekaru 12 da sace ɗaliban Chibok 272, har yanzu ba a san makomar 83 ba
Ya kara da cewa jami’an yansanda a karamar hukumar Babura sunyi arangama da wasu yan bindiga 9 a kauyen Andau dake yankin karamar hukumar.
Sule Gomna ya kuma ce tawagar yansanda ta musamman masu yaki da fashi da makami sun kama mutane 10 da ake zargin barayine yan bindiga a kwaryar birnin Dutse.