‘Yansanda sun fara bincike akan mutuwar Abdulkarim Na Allah

‘Yansanda sun fara bincike akan mutuwar Abdulkarim Na Allah, duk da kasancewar gwamnatin jihar Kaduna ta bayyana lamarin da mai kama da kisan kai.

Mamacin da ne a wajen Sanata Bala Na’Allah.

Kwamishinan yansanda na jihar Kaduna, Mudasiru Abdullahi, ya bayar da umarnin bincike akan lamarin.

Kwamishinan ya bayar da umarnin a daren jiya a Kaduna, cikin wata sanarwa da kakakin yansandan jihar, Mohammed Jalige, ya fitar.

An rawaito cewa an kashe matukin jirgin sama mai shekara 36 jiya a gidansa dake Kaduna.

‘Yansanda sun nemi jama’ar gari da su taimaka da bayanai masu muhimmmanci dangane da binciken kisan kan.

A nasa bangaren, kwamishinan tsaro da harkokin cikin gidan jihar Kaduna, Samuel Aruwan, ya bayyana matsayar gwamnatin jihar cikin wata sanarwa da ya fitar jiya a Abuja.

Comments (0)
Add Comment