Sufeto Janar na Yansanda, Mohammed Adamu, ya jaddada alkawarinsa na yin garanbawul ga tawagar yansanda masu yaki da fashi da mamaki, da sauran bangarorin yansanda na musamman.
Sufeto Janar ya sanar da haka jiya a Abuja lokacin da ministan matasa da wasanni, Sunday Dare, ya kai masa ziyarar ban girma.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa ta hannun kakakin yansanda, Frank Mba.
- An shawarci al’ummar jihar Jigawa su tashi tsaye wajen dasa bishiyoyi da renon su
- Ministan ma’aikatar albarkatun ruwa da tsaftar muhalli ya kaddamar da cibiyar samar da ruwan sha dake garin Birnin Kudu
- Gwamnatin tarayya ta bayyana shirinta na sake duba farashin lasisin hakar ma’adanai
- Sauye-sauyen tattalin arzikin da shugaba Bola Tinubu yayi ne ya fardado da Najeriya daga durkushewa
- An kara kama masu alaka da zanga-zangar goyon bayan Falasdinawa a jami’ar Texas
Sufeto Janar yayi kira ga ‘yan kasa da suyi hakuri, inda yayi nuni da cewa ana cigaba da yin garanbawul ga tawagar yansanda masu yaki da fashi da mamaki.
Ya jaddada cewa an kama wasu daga cikin jami’an yansandan da laifin wuce gona da iri akan yan kasa, musamman matasa, kuma tuni suka fara fuskantar hukunci.
Da yake mayar da jawabi, Sunday Dare ya yabawa Sufeto Janar bisa matakin da ya dauka na gaggawa wajen magance matsalar, inda ya nemi inganta hadin gwiwa da kyakykyawar fahimtar juna tsakanin yansanda da matasa.