Zazzabin Lassa yayi sanadiyyar mutuwar mutane 366 a jihohi 24

Hukumar Dakile Yaduwar Cututtuka ta Najeriya (NCDC) ta sanar da mutuwar mutane 366 daga cututtukan zazzabin Lassa da sankarau a jihohi 24 na ƙasarnan daga watan Janairu zuwa 18 ga watan Mayu.

A cewar rahoton hukumar, an tabbatar da mutum 733 da suka kamu da zazzabin Lassa daga cikin mutane 5,118 da ake zargi da kamuwa a ƙananan hukumomi 95 a jihohi 18, inda cutar ta fi shafar matasa ‘yan shekara 21 zuwa 30.

Cutar ta fi kamari a jihohin Ondo, Bauchi da Edo, wadanda suka haɗa kaso 72 cikin ɗari na duka masu cutar, yayin da cutar sankarau ta fi shafar yara ‘yan shekaru 5 zuwa 14, musamman a arewacin kasa. Hukumar ta ce an kafa Cibiyar Aikin Gaggawa tare da haɗin gwiwar ma’aikatar lafiya, hukumar rigakafi ta kasa da sauran abokan haɗin gwiwa don daƙile yaduwar cututtukan.

Comments (0)
Add Comment