Abba Atiku Ya Ce Babu Wanda Zai Iya Doke Tinubu A Zaben 2027 Ko da Maihaifinsa Ne

Abba Atiku, ɗan tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar, ya bayyana a fili cewa mahaifinsa ba shi da wata damar doke Shugaba Bola Tinubu gabannin zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027.

Abba ya yi wannan furuci ne a ranar Litinin a birnin Yola, Jihar Adamawa, yayin kammala sauya sheƙarsa, inda ya karɓi katin zama ɗan jam’iyyar APC a mazabar Gwadabawa da ke Ƙaramar Hukumar Yola North.

Da yake bayani kan dalilin sauya sheƙarsa, Abba ya nuna abin da ya kira nasarorin gwamnatin Tinubu a ɓangarorin gyaran tattalin arziƙi, bunƙasar ɗan Adam da ci gaban ƙasa baki ɗaya.

Ya ce: “Ina so in bayyana a sarari cewa babu wani mutum ko jam’iyya da za ta iya hana Shugaba Bola Tinubu komawa Aso Rock a 2027.

“’Yan Najeriya sun ga ayyukansa na alheri; ba mai nuna wariya ba ne, ba ya yin naɗe-naɗe bisa addini ko yanki, sai dai bisa cancanta kawai,” in ji shi.

Baya ga nuna goyon bayansa kai tsaye, Abba ya yi kira ga ’yan Najeriya daga kowane ɓangaren jam’iyyu da su mara wa shugaban ƙasa baya, yana mai jaddada buƙatar ci gaba da tafiya a kan aikin da aka fara.

Ya ce: “Shugaban ƙasa na buƙatar goyon bayanku domin ya ci gaba da kyawawan ayyukan da yake yi.”

Shugabannin jam’iyyar APC a Jihar Adamawa sun ɗauki wannan sauya sheƙa a matsayin wata alama ta ƙara ƙarfafa jam’iyyar.

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC na Yankin Adamawa ta Tsakiya, Alhaji Isa Bagalti, wanda ya miƙa wa Abba katin zama ɗan jam’iyya, ya bayyana matakin a matsayin tabbaci cewa APC na da cikakken shiri da matsayi mai ƙarfi domin samun nasara a zaɓen 2027.

Fitaccen jigon APC, Alhaji Jamil Yusuf, ya yi watsi da duk masu tunanin kalubalantar sake zaɓen Tinubu, yana mai kiran su da “masu mafarkin banza” da ba su da nauyin siyasa da zai iya kawar da shugaban ƙasar mai ci.

Abba Atiku ya sauya sheƙa zuwa jam’iyyar All Progressives Congress a ranar 15 ga Janairu, inda Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, da Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa (Arewa Maso Gabas), Mustapha Salihu, suka tarbe shi.

Comments (0)
Add Comment