Mataimakin Shugaban Kasa Yemi Osinbajo ya amince da cewa miliyoyin ‘yan Najeriya na fama da bakin talauci.
Yace shugabannin da aka zaba a yanzu, zasu zama na jeka na yi ka matukar basu hada kai ba wajen magance abinda da ya kira matsalolin dake neman tarwatsa kasarnan ba.
Osinbajo ya fadi hakan ne yayin bikin rufe taron wuni biyu tsakanin bangaren zartarwa da majalisa wanda aka gudanar a fadar shugaban kasa dake Abuja.
- An kara kama masu alaka da zanga-zangar goyon bayan Falasdinawa a jami’ar Texas
- Gwamnan jihar Zamfara ya yi alkawarin tsai da kudurin magance ma’aikatan da ke karbar albashi da yawa a jihar
- Kifewar jirgin ruwa yayi sanadiyyar mutuwar wasu dalibai 2 a jihar Kano
- Tinubu ya nuna rashin jindadinsa kan mafi karacin albashi na Naira 615,000
- Burkina Faso ta dakatar da wasu kafafen watsa labarai da dama na Ƙasashen Yamma har sai baba ta gani
Yace akwai bukatar yan bangaren zartarwa da yan majalisa su hada kai muddin suna gudun bawa yan Najeriya kunya, wadanda suka basu damar rike mukaman siyasa a manyan matakai.
A takardar bayan taro da aka fitar a karshe taron, wadanda suka halarci taron, sun nemi a samar da shiri mai inganci na sansanta juna tsakanin bangaren zartarwa da na majalisa, domin cigaban kasa.