ASUU Ta Gargadi Gwamnati Kan Yiwuwar Sake Shiga Yajin Aiki

Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya, ASUU, ta yi barazanar sake shiga yajin aiki sakamakon abin da ta bayyana a matsayin gazawar gwamnatin tarayya wajen cika yarjejeniyar da aka cimma a shekarar 2025.

Ƙungiyar ta bayyana cewa gwamnatin ta kasa aiwatar da muhimman alkawuran da suka shafi biyan haƙƙoƙin malamai, inganta walwalar ma’aikata da kuma bunƙasa harkokin jami’o’in gwamnati a faɗin ƙasar nan.

ASUU ta kuma yi gargadin cewa idan ba a ɗauki matakin gaggawa ba domin warware matsalolin da ake fuskanta, hakan na iya janyo tsaikon karatu a jami’o’in Najeriya.

Kungiyar ta bukaci gwamnatin tarayya da ta mutunta yarjejeniyoyin da aka cimma domin kaucewa sake fadawa rikicin yajin aikin da kan shafi ɗalibai da tsarin ilimi baki ɗaya.

Comments (0)
Add Comment