Gwamnan jihar Jigawa Muhammadu Badaru Abubakar ya amince da tura Alhaji Bala Ibrahim Mamsa a matsayin sabon kwamishina a ma’aikatar yada labarai, matasa, wassani da al’adu ta jiha.
Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa dauke da sa hannun sakataren gwamnatin jiha, Alhaji Adamu Abdulkadir Fanini, wacce aka rabawa manema labarai a Dutse.
- Ya Kamata A Kyautata Rayuwar Talaka Bayan Cire Tallafin Mai – Atiku
- An Kama Mai Safarar Bindigogi A Tashar Mota A Zariya
- Alƙawarin Atiku Na Dawo da Tallafin Mai Ya Jawo Muhawara A Jigawa
- Tun da Na Zama Gwamnan Kaduna Ban Karɓi Bashin Sisin Kobo Ba – Uba Sani
- ’Yan Bindiga Sun Kashe Malami, Sun Sace Mutum 10 A Sakkwato
Sanarwar tace gwamnan ya kuma amince da canja Alhaji Muhammad Alhassan daga ma’aikatar yada labarai, matasa, wassani da al’adu zuwa ma’aikatar aikin gona da ma’adanan kasa, a matsayin kwamishina.
Sanarwar ta yi kira ga kwamishinonin da su sadaukar da kawunansu wajen tabbatar da samun nasarar kudirori da tsare-tsaren gwamnatin Badaru, domin cigaban jihar baki daya.