Hukumar Civil Defence ta yi gargadi kan amfani da wuta a lokutan bukukuwan Kirsimeti

Hukumar kare fararen hula da civil defence ta yi gargadi kan amfani da wuta a lokutan bukukuwan Kirsimeti da na sabuwar shekara.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai a Dutse, mai dauke da sa hannun mai magana da yawun hukumar a jihar Jigawa, Adamu Shehu.

Adamu Shehu ya shawarci al’ummar jiharnan da su kara taka tsantsan da kuma kula da harkokin tsaro a yayin bukukuwan.

Ya bayyana cewa, a shirye-shiryen da ake yi na gudanar da bukukuwan Kirsimeti da na sabuwar shekara a Jihar Jigawa, Kwamandan hukumar a Jihar, Mustapha Talba, ya kuma bayar da umarnin tura jami’ai 750 cikin gaggawa domin ganin an gudanar da bukukuwan lami lafiya a fadin kananan hukumomin jiharnan 27.

Ya kuma yi kira ga al’ummar jiharnan da su kara taka tsan-tsan, su zama masu bin doka da oda, tare da kai rahoton duk wani abu bakon abu da basu yarda da shi ba, zuwa ga hukumar tsaro mafi kusa.

Comments (0)
Add Comment