Kimanin Masu karamin karfi dubu daya da dari biyar da talatin da hudu ne da aka zabo daga garuruwa goma sha biyar a yankin karamar hukumar Birniwa zasu amfana da tallafin naira dubu biyar-biyar karkashin shirin rage radadin talauci na kasa.
Manajan ofishin shirin biyan kudade na jiha, Kabiru Yahaya Abdulkadir, ya bayyana haka lokacin raba koren katin karbar tallafin a sakatariyar karamar hukumar Birniwa.
- Sarki Charles zai koma aiki makon gobe
- Amurka ta bayar da bayanin tallafin soji na $6Bn da ta bai wa Ukriane
- Japan za ta taimakawa ƙananan ma’aikata a Najeriya domin samar da shinkafa
- Gwamnatin Jigawa ta jadadda kudirinta na daukar kwararan matakai na rage talauci a jihar
- An kama haramtattun nakiyoyi 6,240 a hanyar Yauri zuwa Jega da ke Jihar Kebbi
A nasa jawabin shugaban karamar hukumar wanda ya samu wakilcin mataimakinsa Alhaji Umar Baffa ya yabawa gwamnatin shugaban kasa Muhammad Buhari bisa bada tallafi ga masu karamin karfi.
Tunda farko a jawabinsa jami’in kula da shirin na karamar hukumar, Shehu Baba Birniwa ya ce wannan shi ne karon farko da al’ummar karamar hukumar zasu ci gajiyar shirin.