Kusan Mutane 2000 sun rabauta da Tallafin Gwamnatin Tarayya na 5000 a Birniwa

Kimanin Masu karamin karfi dubu daya da dari biyar da talatin da hudu ne da aka zabo daga garuruwa goma sha biyar a yankin karamar hukumar Birniwa zasu amfana da tallafin naira dubu biyar-biyar karkashin shirin rage radadin talauci na kasa.

Manajan ofishin shirin biyan kudade na jiha, Kabiru Yahaya Abdulkadir, ya bayyana haka lokacin raba koren katin karbar tallafin a sakatariyar karamar hukumar Birniwa.

A nasa jawabin shugaban karamar hukumar wanda ya samu wakilcin mataimakinsa Alhaji Umar Baffa ya yabawa gwamnatin shugaban kasa Muhammad Buhari bisa bada tallafi ga masu karamin karfi.

Tunda farko a jawabinsa jami’in kula da shirin na karamar hukumar, Shehu Baba Birniwa ya ce wannan shi ne karon farko da al’ummar karamar hukumar zasu ci gajiyar shirin.

JigawaMuhammad Badaru AbubakarMuhammadu Buhari
Comments (0)
Add Comment