Sarkin Kano, Mai Martaba Alhaji Aminu Ado Bayero, ya yabawa gwamna Muhammadu Badaru Abubakar bisa aiwatar da ayyukan raya kasa a jihar Jigawa.
Ya sanar da haka lokacin da ya kaiwa gwamnan ziyara a gidan gwamnatin dake Dutse.
Sarkin ya bayyana cewa yayin ziyararsa zuwa masarautun jiharnan, ya yaba da ayyukan da suka kawata birane da yankunan karkara a fadin jihar.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
- Ma’aikatan Abuja Ba Sa Sona — Wike
Aminu Ado Bayero ya gayawa gwamnan cewa yazo jihar ne domin gabatar da kansa tare da neman shawarwarin sarakunan, inda ya godewa mutanen jiharnan bisa kyakykyawar tarbar da suka yi masa.
Da yake mayar da martani, Gwamna Badaru Abubakar yace yayi farinciki da alfahari da ziyarar sarkin, wacce yace zata karfafa danganta mai kyau da tarihi tsakanin mutanen jihoshin Kano da Jigawa.