Yadda akai yan bindiga su kai hari kan jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja

Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun kai hari kan jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja, lamarin da ya tilasta wa jirgin ya tsaya a tsakiyar hanya.

An raiwaito cewa yan bindigan sun fara kai farmaki kan jirgin a jiya da daddare kuma sun samu nasarar tsayar da shi.

‘Yan bindigar, a cewar majiya, sun sake dawowa da safiyar yau, inda suka dasa nakiyoyi akan hanyar jirgin kasa.

Wani ma’aikacin Hukumar Jiragen Kasa da ya nemi a sakaye sunansa, ya sanar da cewa sun fuskanci harbe-harbe, kuma jirgin ya tsaya yayin da harbe-harben suka lalata tankin mai.

Hukumar Jiragen Kasa kazalika ta tabbatar da cewa nakiyoyin da aka dasa sun tashi akan hanyar jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja, amma ba a san wadanda suka dasa ba.

Manajan daraktan hukumar, Fidet Okhiria, wanda ya zanta da manema labarai ya bayyana cewa abubuwan fashewar sun lalata digar jirgin.

Comments (0)
Add Comment