Shugaban Sojojin Kasa, Laftanal Janar Tukur Burutai yayi gargadin cewa sojoji baza su kyale bata gari su tarwatsa zaman lafiyar Najeriya ba.
Mukaddashin daraktan hulda da jama’a na hukumar soji, Kanal Sagir Musa, yace Buratai ya fadi hakan a jiya yayin zaman ganawa da manyan jami’an soji da kwamandojin barikoki da na filin yaki, wanda aka gudanar a Abuja.
Sagir Musa ya yiwa yan jarida jawabi akan abin da aka tattauna a zaman ganawar, lokacin da yake zantawa da manema labarai.
Tukur Buratai ya gayawa manyan jami’an soji da kwamandojin barikoki da na filin yaki cewa babu hurumin rashin biyayya tsakankanin dukkan jami’ai da sojojin Najeriya.
- Airtel ta dakatar da bayar da bashin kati da data a Najeriya
- ’Yan adawa ba su isa su razanar da ni ba – Tinubu
- Sojoji sun kama masu satar man fetur a Legas, sun kama mutum 14
- Talauci ya ragu daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto
- Bayan shekaru 12 da sace ɗaliban Chibok 272, har yanzu ba a san makomar 83 ba
Ya bayar da umarnin cewa dole su jaddadawa na kasa da su cewa hukumar soji ta jajirce wajen tabbatar da dorewar mulkin demokradiyya a Najeriya, kasancewar ita ce hanya daya tilo wajen samar da cigaba.