Gwamnatin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ta amince da kafa wata sabuwar hukuma da zata yaki cin hanci da rashawa.
Sabuwar hukumar wacce majalisar zartarwa ta tarayya ta amince da ita, za a dora mata nauyin kula da dukkan kadarorin satar da aka kwato.
Ministan shari’ah kuma babban lauyan tarayya, Abubakar Malami, ya sanar da haka ga manema labaran fadar shugaban kasa, bayan zaman ganawar majalisar zartarwa ta tarayya wanda aka gudanar a jiya laraba.
- Airtel ta dakatar da bayar da bashin kati da data a Najeriya
- ’Yan adawa ba su isa su razanar da ni ba – Tinubu
- Sojoji sun kama masu satar man fetur a Legas, sun kama mutum 14
- Talauci ya ragu daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto
- Bayan shekaru 12 da sace ɗaliban Chibok 272, har yanzu ba a san makomar 83 ba
Yace sabuwar hukumar za ta sake bibiyar yadda ake kula da kadarori da dukiyoyin da aka kwato daga hannun marasa gaskiya.
Ministan yace majalisar zartarwa ta tarayya ta amince da aikawa da kudirin neman kafa hukumar zuwa ga majalisar kasa.