Gwamnatin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ta amince da kafa wata sabuwar hukuma da zata yaki cin hanci da rashawa.
Sabuwar hukumar wacce majalisar zartarwa ta tarayya ta amince da ita, za a dora mata nauyin kula da dukkan kadarorin satar da aka kwato.
Ministan shari’ah kuma babban lauyan tarayya, Abubakar Malami, ya sanar da haka ga manema labaran fadar shugaban kasa, bayan zaman ganawar majalisar zartarwa ta tarayya wanda aka gudanar a jiya laraba.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
Yace sabuwar hukumar za ta sake bibiyar yadda ake kula da kadarori da dukiyoyin da aka kwato daga hannun marasa gaskiya.
Ministan yace majalisar zartarwa ta tarayya ta amince da aikawa da kudirin neman kafa hukumar zuwa ga majalisar kasa.