Shugaban kasar yayi kira ga masu ruwa da tsaki a zaben da za a gudanar a gobe Asabar da su kauracewa abinda ya kira, ko a mutu ko ayi rai.
Matsayar Shugaba Buhari na kunshe cikin wata sanarwa wacce kakakinsa, Garba Shehu, ya fitar.
- Gwamnatin Jigawa zata cigaba da tallafawa Jami’ar Fasaha ta gwamnatin tarayya dake garin Babura
- Aƙalla mutum 42 ne suka mutu sakamakon ƙyanda a jihar Adamawa
- Gwamnan Jihar Gombe ya yi kira ga sabbin zababbun shugabannin kananan hukumomi da su yi aiki tukuru
- Gwamna Dikko Radda ya kare ziyarar da gwamnonin Arewa suka kai kasar Amurka
- Kasar Turkiyya ta dakatar da duk wata hulɗar kasuwanci da Isra’ila
Garba Shehu ya rawaito Buhari yana cewa ya jajirce matuka akan gudanar da zaben gaskiya da adalchi, amma jajircewarsa baza ta isa ba muddin masu aikin zaben suka ki kiyayewa da dokoki.
Shugaban kasar ya kara da cewa yana so yaga an dabbaka tsarin demokradiyya a kasarnan.