Dalilan da yasa gwamnatin tarayya ta kaddamar da kudin intanet na eNaira

Kudin internet na babban bankin kasa (CBN) mai suna eNaira ya fara aiki bayan shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar da shi yau a hukumance.

An kaddamar da kudin a fadar shugaban kasa dake Abuja. A baya an dage shirin kaddamar da kudin na internet a ranar 1 ga watan Oktoba.

Najeriya daya ce daga cikin kasashe kalilan a duniya wadanda suka kirkiri kudin internet.

Wani kamfanin Bitt ne ya samar da eNaira, kamfanin kuma shine wanda ya samar da kudaden internet na wasu kasashen nahiyar kudancin Amurka.

A wajen bikin kaddamarwar a yau, gwamnan babban bankin kasa (CBN), Godwin Emefiele, yace tuni aka samar da kudin eNaira miliyan 500.

Tuni aka fara sauko da manhajojin asusun kudin na internet a wayoyin android da iphone.

Wani bayani a shafin internet na eNaira ya bayyana yadda kudin da asusunsa za suyi aiki.

Comments (0)
Add Comment