Dalilan da yasa gwamnatin tarayya ta kaddamar da kudin intanet na eNaira

0 57

Kudin internet na babban bankin kasa (CBN) mai suna eNaira ya fara aiki bayan shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar da shi yau a hukumance.

An kaddamar da kudin a fadar shugaban kasa dake Abuja. A baya an dage shirin kaddamar da kudin na internet a ranar 1 ga watan Oktoba.

Najeriya daya ce daga cikin kasashe kalilan a duniya wadanda suka kirkiri kudin internet.

Wani kamfanin Bitt ne ya samar da eNaira, kamfanin kuma shine wanda ya samar da kudaden internet na wasu kasashen nahiyar kudancin Amurka.

A wajen bikin kaddamarwar a yau, gwamnan babban bankin kasa (CBN), Godwin Emefiele, yace tuni aka samar da kudin eNaira miliyan 500.

Tuni aka fara sauko da manhajojin asusun kudin na internet a wayoyin android da iphone.

Wani bayani a shafin internet na eNaira ya bayyana yadda kudin da asusunsa za suyi aiki.

Leave a Reply

%d bloggers like this: