Gwamnan Jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya saki fursunoni 293 wanda suke tsare a gidajen gyaran Da’a a jihar ta Kano.
Sakin nasu yazo ne bayan umarnin da gwamnatin tarayya ta bawa Jihohi, kan su rage Cunkoso a gidajen gyaran da’ar, saboda annobar Coronavirus.
- Gwamnatin Jigawa zata cigaba da tallafawa Jami’ar Fasaha ta gwamnatin tarayya dake garin Babura
- Aƙalla mutum 42 ne suka mutu sakamakon ƙyanda a jihar Adamawa
- Gwamnan Jihar Gombe ya yi kira ga sabbin zababbun shugabannin kananan hukumomi da su yi aiki tukuru
- Gwamna Dikko Radda ya kare ziyarar da gwamnonin Arewa suka kai kasar Amurka
- Kasar Turkiyya ta dakatar da duk wata hulɗar kasuwanci da Isra’ila
Mai magana da yawun Rundunar hukumar Gyaran Da’ar na Jihar Kano DSC Musbahu Lawan Nassarawa, shine ya tabbatar da sakin Fursunonin cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai.
DSC Lawan, ya bayyana cewa gwamnan Jihar ta Kano ya biya kudi kimanin Naira Miliyan 12 ga Fursunonin tare da basu naira dubu 5 domin suyi kudin Mota zuwa gida.
Kazalika ya bukaci Fursunonin da aka saka su kasance masu canza halaiyar su, saboda damar da aka basu na zama mutanen kirki.