Gwamnan Jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya saki fursunoni 293 wanda suke tsare a gidajen gyaran Da’a a jihar ta Kano.
Sakin nasu yazo ne bayan umarnin da gwamnatin tarayya ta bawa Jihohi, kan su rage Cunkoso a gidajen gyaran da’ar, saboda annobar Coronavirus.
- Airtel ta dakatar da bayar da bashin kati da data a Najeriya
- ’Yan adawa ba su isa su razanar da ni ba – Tinubu
- Sojoji sun kama masu satar man fetur a Legas, sun kama mutum 14
- Talauci ya ragu daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto
- Bayan shekaru 12 da sace ɗaliban Chibok 272, har yanzu ba a san makomar 83 ba
Mai magana da yawun Rundunar hukumar Gyaran Da’ar na Jihar Kano DSC Musbahu Lawan Nassarawa, shine ya tabbatar da sakin Fursunonin cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai.
DSC Lawan, ya bayyana cewa gwamnan Jihar ta Kano ya biya kudi kimanin Naira Miliyan 12 ga Fursunonin tare da basu naira dubu 5 domin suyi kudin Mota zuwa gida.
Kazalika ya bukaci Fursunonin da aka saka su kasance masu canza halaiyar su, saboda damar da aka basu na zama mutanen kirki.