Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya bayyana damuwa bisa karuwar cin zarafin mata, musamman fyade a jihar, inda yayi alkawarin sanya dandaka a cikin sabuwar dokar cin zarafin bil’adama wacce ya sanyawa hannu kwanannan.
Bala Mohammed ya fadi haka lokacin da ya karbi bakuncin ministar harkokin mata da cigaban yara, Pauline Tallen, wacce ta kai masa ziyarar aiki jiya a gidan gwamnati dake Bauchi.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
Gwamnan yace za a mayar da dokar cin zarafin bil’adama zuwa majalisar dokokin jihar, domin tabbatar da an gyare-gyare a inda aka samu sabani.
Tunda farko, a jawabinta, ministar harkokin mata da cigaban yara, Pauline Tallen, ta bayyana fyade a matsayin abinda yafi kisan kai muni.