Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya bayyana damuwa bisa karuwar cin zarafin mata, musamman fyade a jihar, inda yayi alkawarin sanya dandaka a cikin sabuwar dokar cin zarafin bil’adama wacce ya sanyawa hannu kwanannan.
Bala Mohammed ya fadi haka lokacin da ya karbi bakuncin ministar harkokin mata da cigaban yara, Pauline Tallen, wacce ta kai masa ziyarar aiki jiya a gidan gwamnati dake Bauchi.
- Amurka ta ce jami’anta na ganawa da sojojin da ke mulki a Jamhuriyar Nijar
- Gwamnatin jihar Jigawa ta fito da wani shiri na amfani da fasaha wajen koyo da koyarwa a jihar
- Kungiyar NULGE reshen karamar Hukumar Buji ta yabawa wakilin mazabar Buji a majalisar dokoki
- Aƙalla fursunoni 118 ne suka tsere daga gidan yarin Suleja
- Kasashen Afirka sun amince su yi magana da murya daya domin yaki da ta’addanci
Gwamnan yace za a mayar da dokar cin zarafin bil’adama zuwa majalisar dokokin jihar, domin tabbatar da an gyare-gyare a inda aka samu sabani.
Tunda farko, a jawabinta, ministar harkokin mata da cigaban yara, Pauline Tallen, ta bayyana fyade a matsayin abinda yafi kisan kai muni.