Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya bayyana damuwa bisa karuwar cin zarafin mata, musamman fyade a jihar, inda yayi alkawarin sanya dandaka a cikin sabuwar dokar cin zarafin bil’adama wacce ya sanyawa hannu kwanannan.
Bala Mohammed ya fadi haka lokacin da ya karbi bakuncin ministar harkokin mata da cigaban yara, Pauline Tallen, wacce ta kai masa ziyarar aiki jiya a gidan gwamnati dake Bauchi.
- Gwamnatin Gombe Ta Ware N260m Don Sauya Wa Kasuwar Hatsi Matsuguni
- TUC Za Ta Karfafa Haɗin Gwiwa da Gwamnatin Jigawa Don Walwalar Ma’aikata
- Mutum 3,000 Sun Yi Hijira Saboda Hare-Haren ’Yan Bindiga A Katsina
- An Kama Jami’in DSS Na Bogi A Abuja
- Davido Aka So Kashewa A Harin da Aka Kai Wa Tawagar Adeleke — ’Yan Sanda
Gwamnan yace za a mayar da dokar cin zarafin bil’adama zuwa majalisar dokokin jihar, domin tabbatar da an gyare-gyare a inda aka samu sabani.
Tunda farko, a jawabinta, ministar harkokin mata da cigaban yara, Pauline Tallen, ta bayyana fyade a matsayin abinda yafi kisan kai muni.